Manzon Allah (ﷺ) yace: “Ku roƙi Allah kuna masu sakankancewa da amsawa”.
Wannan Hadisi yana koya mana mahimmacin roƙon Allah ta’ala da kuma sakin jiki da cewa Allah zai amsa addu’a ba tare da kokwanto ba. Allah yana da kirki, Allah mawadacine, Allah bashi da rowa, Allah yana jinka, Allah yana ganinka, Allah yasan halin da kake ciki. Allah ka Amsa buƙatarmu ka yaye damuwarmu.